Skip to content
Ayuba 33:14-30

Ayuba 33:14-30

14
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da ’yan aikan mutuwa.
23
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options