Skip to content
Ayuba 33:12-18

Ayuba 33:12-18

12
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options