Skip to content
Ayuba 30:20

Ayuba 30:20

Ana nuna aya 20 tare da mahallin da ke kewaye.
17
Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
18
A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
19
Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
20
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
Settings

Reading style

Typeface

Font size 19px

Reading width 90 chars

Options