Skip to content
Ayuba 30:20-24

Ayuba 30:20-24

20
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
24
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options