Ayuba 3:20-26
20
“Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
21
ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
22
waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
23
Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
24
Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
25
Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
26
Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”
Settings