Skip to content
Ayuba 3:11-16

Ayuba 3:11-16

11
“Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
12
Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
13
Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
14
tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
15
da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
16
Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options