Ayuba 28:20-28
20
“To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
21
An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
22
Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
23
Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
24
Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
25
Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
26
Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
27
sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
28
Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’ ”
Settings