Ayuba 27:13-20
13
“Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
14
Kome yawan ’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
15
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
16
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
17
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
18
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
19
Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
20
Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
Settings