Ayuba 22:15-18
15
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Settings