Ayuba 22:12-20
12
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
13
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
14
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
15
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
19
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
20
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
Settings