Ayuba 15:7-10
7
“Kai ne mutum na farko da aka fara haihuwa? Ko kai ne aka fara halitta kafin tuddai?
8
Kana sauraron shawarar Allah? Ko kana gani kai kaɗai ne mai hikima?
9
Me ka sani da ba mu sani ba? Wane fahimi kake da shi da ba mu da shi?
10
Masu furfura da tsofaffi suna gefenmu mutanen da sun girme babanka.