Irmiya 51:40-44
40
“Zan sauko da su kamar tumaki zuwa mayanka, kamar raguna da bunsurai.
41
“Yadda za a ci Sheshak, taƙamar duniya duka za tă daina! Babilon za tă zama abar ƙyama a cikin al’ummai!
42
Teku zai malalo a kan Babilon, raƙumansa masu hauka za su rufe ta.
43
Garuruwanta sun zama abin kufai, za tă zama hamada inda ba ruwa, ƙasar da ba mazauna, ba kuma mutumin da zai ratsa ta cikinta.
44
Zan hukunta Bel a Babilon, in sa ya yi aman abin da ya haɗiye. Ƙasashe ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Katangan Babilon kuwa za tă rushe!
Settings