Irmiya 41:4-5
4
Kashegari bayan an kashe Gedaliya, kafin wani ya san abin da ya faru,
5
sai ga mutane tamanin daga Shekem, Shilo da Samariya suka zo da gemunsu a aske, da tufafinsu a kece, da jikunansu a tsage, suka kawo hadayun gari da turare tare da su a gidan Ubangiji.