Irmiya 18:1-4
1
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
2
“Ka gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, a can zan ba ka saƙona.”
3
Sai na gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, na gan shi yana aiki a na’urar ginin tukwanen.
4
Amma tukunyar da yake ginawa ta lalace a hannuwansa, sai mai ginin tukwanen ya sāke gina wata tukunya dabam, yana gyara ta yadda ya ga dama.
Settings