Skip to content
Ishaya 7:10-16

Ishaya 7:10-16

10
Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
11
“Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.”
12
Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
13
Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
14
Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
15
In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
16
Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options