Skip to content
Ishaya 38:1-3

Ishaya 38:1-3

1
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
2
Hezekiya ya juye fuskarsa wajen bango ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
3
“Ka tuna, ya Ubangiji, yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da dukan zuciya na kuma yi abin da yake nagari a idanunka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options