Ishaya 30:30-31
30
Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
31
Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.