Skip to content
Hosiya 5:8-12

Hosiya 5:8-12

8
“Amon kakaki a Gibeya, ƙaho a Rama. Ku yi kirarin yaƙi a Bet-Awen; ku ja gaba, ya Benyamin.
9
Efraim za tă zama kango a ranar hukunci. A cikin kabilan Isra’ila na yi shelar abin da yake tabbatacce.
10
Shugabannin Yahuda suna kamar waɗanda suke matsar da duwatsun shaidar da aka sa a kan iyaka ne. Zan zubo musu da fushina a kansu kamar rigyawar ruwa.
11
An danne Efraim, an murƙushe ta a shari’a ta ƙudura ga bin gumaka.
12
Na zama kamar asu ga Efraim, kamar ruɓa ga mutanen Yahuda.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options