Skip to content
Ibraniyawa 11:13-16

Ibraniyawa 11:13-16

13
Duk mutanen nan suna cikin bangaskiya sa’ad da suka mutu. Ba su kuwa karɓi abubuwan da aka yi alkawari ba; sun dai hango su suka kuma marabce su daga nesa. Suka kuma amince cewa su baƙi ne, bare kuma a duniya.
14
Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu.
15
Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa.
16
A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options