Skip to content
Haggai 1:2-8

Haggai 1:2-8

2
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’ ”
3
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
4
“Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
5
To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
6
Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
7
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
8
Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options