Farawa 6:9-13
9
Ga tarihin Nuhu. Nuhu mutum ne mai adalci, marar abin zargi a cikin mutanen zamaninsa, ya kuma yi tafiya tare da Allah.
10
Nuhu yana da ’ya’ya maza uku, Shem, Ham da Yafet.
11
Duniya dai ta lalace sosai a gaban Allah, ta kuma cika da tashin hankali.
12
Allah ya ga yadda duniya ta lalace, gama dukan mutane a duniya sun lalatar da rayuwarsu.
13
Saboda haka, Allah ya ce wa Nuhu, “Zan kawo ƙarshen dukan mutane, gama saboda su duniya ta cika da tashin hankali. Lalle zan hallaka su da kuma duniya.
Settings