Naar de inhoud
Farawa 31:45-49

Farawa 31:45-49

45
Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
46
Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
47
Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
48
Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
49
Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options