Skip to content
Farawa 28:18-22

Farawa 28:18-22

18
Kashegari da sassafe, sai Yaƙub ya ɗauki dutsen da ya yi matashin kai da shi, ya kafa shi al’amudi, ya kuma zuba mai a kansa.
19
Ya kira wannan wuri Betel ko da yake dā ana kiran birnin Luz ne.
20
Sa’an nan Yaƙub ya yi alkawari cewa, “In Allah zai kasance tare da ni yă kuma lura da ni a wannan tafiya, yă kuma ba ni abinci in ci da tufafi in sa,
21
har in dawo lafiya zuwa gidan mahaifina, to, Ubangiji zai zama Allahna
22
kuma wannan dutsen da na kafa al’amudi, zai zama gidan Allah, kuma dukan abin da ka ba ni zan ba ka kashi ɗaya bisa goma.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options