Skip to content
Farawa 17:23-27

Farawa 17:23-27

23
A wannan rana, Ibrahim ya ɗauki ɗansa Ishmayel da dukan waɗanda aka haifa cikin gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗinsa, ya kuwa yi wa kowane namiji a cikin gidansa kaciya kamar yadda Allah ya faɗa masa.
24
Ibrahim yana da shekara tasa’in da tara sa’ad da aka yi masa kaciya,
25
Ishmayel ɗansa kuma yana da shekara goma sha uku.
26
Aka yi wa Ibrahim da ɗansa Ishmayel kaciya a rana ɗaya.
27
Aka yi wa kowane namiji a gidan Ibrahim kaciya, da waɗanda aka haifa a gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗi daga baƙo.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options