Farawa 1:1-3
1
A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
2
To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
3
Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.