Skip to content
Galatiyawa 5:2

Galatiyawa 5:2

Ana nuna aya 2 tare da mahallin da ke kewaye.
1
Saboda ’yanci ne Kiristi ya ’yantar da mu. Sai ku tsaya daram, kada ku yarda ku sāke komawa ƙarƙashin nauyin bauta.
2
Ku lura da kalmomina! Ni Bulus ina gaya muku cewa in kuka yarda aka yi muku kaciya, wannan ya nuna Kiristi ba shi da amfani a gare ku ba ko kaɗan.
3
Haka kuma ina ƙara sanar wa kowane mutumin da ya yarda aka yi masa kaciya cewa dole yă kiyaye dukan Doka.
4
Ku da kuke ƙoƙarin kuɓuta ta wurin Doka an raba ku da Kiristi ke nan; kuka kuma fāɗi daga alheri.
5
Amma ta wurin bangaskiya muna marmarin jira adalcin da muke bege ta wurin Ruhu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options