Skip to content
Fitowa 5:6-9

Fitowa 5:6-9

6
A wannan rana Fir’auna ya ba da wannan umarni wa shugabannin masu gandu,
7
“Kada ku ƙara ba wa mutanen ciyawar tattaka domin su yi tubula, bari su tafi su tattara tattaka da kansu.
8
Ku kuma bukace su su yi tubula daidai yawan tubalin da suka saba yi, kada ku rage. Ragwaye ne, shi ya sa suke kuka cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya ga Allahnmu.’
9
Ku sa waɗannan mutane su yi aiki mai tsanani sosai, don kada su sami zarafin kasa kunne ga maganganun ƙarya.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options