Skip to content
Fitowa 31:1-6

Fitowa 31:1-6

1
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
2
“Duba, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuda,
3
na kuma cika shi da Ruhun Allah, fasaha, azanci, da kuma sani cikin kowace irin sana’a,
4
don yin zāne-zāne na aikin zinariya, azurfa da tagulla,
5
don yanka da shirya duwatsu, yin aikin katako, da kuma yin kowane irin aikin sana’ar hannu.
6
Ban da haka, na zaɓi Oholiyab ɗan Ahisamak, na kabilar Dan, don yă taimake shi. Na kuma ba da fasaha ga dukan masu aikin sana’ar hannu, don yin duk abin da na umarce ka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options