Skip to content
Fitowa 25:1-7

Fitowa 25:1-7

1
Ubangiji ya ce wa Musa,
2
“Ka faɗa wa Isra’ilawa su kawo mini hadaya. Za ka karɓi hadaya daga hannun kowane mutum wanda zuciyarsa ta yarda yă bayar.
3
“Ga iri jerin kayan da za ka karɓo daga hannunsu, “zinariya, da azurfa, tagulla,
4
shuɗi, shunayya da jan zare, lallausan lilin, da gashin akuya,
5
fatun ragunan da aka wanke, fatun awaki masu kyau, itacen akashiya,
6
mai domin fitila, kayan yaji domin man keɓewa da kuma turare mai ƙanshi,
7
da duwatsun Onis, da duwatsun da za a mammanne a efod da ƙyallen maƙalawa a ƙirji.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options