21
“Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
22
“Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
23
In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
24
Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye, ’ya’yanku kuwa su zama marayu.