Fitowa 21:22-25
22
“Idan mutum biyu suna faɗa, har suka yi wa mace mai ciki rauni, har ya sa ta yi ɓari, amma wani lahani bai same ta ba, za a ci wa wanda ya yi mata raunin tara bisa ga yadda mijinta ya yanka za a biya, in dai abin da ya yanka ya yi daidai da abin da alƙalai suka tsara.
23
Amma in akwai rauni mai tsanani, sai a ɗauki rai a maimakon rai,
24
ido don ido, haƙori don haƙori, hannu don hannu, ƙafa don ƙafa,
25
ƙuna don ƙuna, rauni don rauni, ƙujewa don ƙujewa.
Settings