Skip to content
Fitowa 16:1-3

Fitowa 16:1-3

1
Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
2
A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
3
Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options