Fitowa 12:49-51
49
Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta shafi ɗan ƙasa da kuma baƙon da yake zama a tsakaninku.”
50
Dukan Isra’ilawa suka yi na’am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
51
A wannan rana, Ubangiji ya fito da Isra’ilawa ɓangare-ɓangare daga Masar.