Skip to content
Mai Hadishi 9:13-16

Mai Hadishi 9:13-16

13
Na kuma ga wani misali game da hikima a duniya wanda ya burge ni sosai.
14
An yi wani ɗan ƙaramin birni mai mutane kaɗan a ciki. Sai wani babban sarki ya kawo masa yaƙi, ya kafa masa babban sansani.
15
A cikin birnin nan kuwa akwai wani mutum matalauci amma mai hikima, ya kuma ceci birnin ta wurin hikimarsa. Amma ba wanda ya tuna da matalaucin nan.
16
Sai na ce, “Hikima ta fi ƙarfe ƙarfi.” Amma aka rena hikimar matalaucin, ba a ma jin maganarsa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options