Tsallake zuwa abun ciki
Maimaitawar Shari’a 5:1-5

Musa ya tunasar da alkawarin Horeb

Maimaitawar Shari’a 5:1-5
1
Musa ya tattara dukan Isra’ila ya ce, Ku ji, ya Isra’ila, ƙa’idodi da dokokin da na furta a kunnuwanku a yau. Ku koye su, ku kuma tabbata kun bi su.
2
Ubangiji Allahnmu ya yi alkawari da mu a Horeb.
3
Ba da kakanninmu ba ne Ubangiji ya yi wannan alkawari, amma da mu ne, da dukanmu waɗanda muke da rai a yau.
4
Ubangiji ya yi magana fuska da fuska da ku daga wuta a kan dutse.
5
(A wannan lokaci na tsaya tsakanin Ubangiji da ku, don in furta muku maganar Ubangiji, domin kun ji tsoron wutar, ba ku kuwa hau dutsen ba.) Ya ce,
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options