Skip to content
Maimaitawar Shari’a 32:26-33

Maimaitawar Shari’a 32:26-33

26
Na ce zan watsar da su in sa a manta da su a tunanin ’yan adam.
27
Amma ina tsoron tsokanar abokin gāba, don kada abokan gāba su kāsa ganewa har su ce, ‘Hannunmu ne ya yi nasara; ba Ubangiji ne ya aikata dukan wannan ba.’ ”
28
Al’ummai ne marasa azanci, babu ganewa a cikinsu.
29
A ce su masu hikima ne har su gane wannan su gane abin da ƙarshensu zai zama!
30
Yaya mutum guda zai kore dubu, mutum biyu su sa dubu goma su gudu, sai ko Dutsensu ya sayar da su, sai ko Ubangiji ya bashe su.
31
Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne, abokan gābanmu sun san da haka.
32
Kuringarsu ta fito daga kuringar Sodom ne, daga gonakin Gomorra kuma. ’Ya’yan inabinsu dafi ne, nonnansu masu ɗaci ne.
33
Ruwan inabinsu dafin macizai ne, mugun dafin gamshaƙa ne.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options