Skip to content
Maimaitawar Shari’a 31:2

Maimaitawar Shari’a 31:2

Ana nuna aya 2 tare da mahallin da ke kewaye.
1
Sai Musa ya fita ya kuma faɗa waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila cewa,
2
“Yanzu shekaruna ɗari da ashirin ne, ba na iya kaiwa da komowa. Ubangiji ya ce mini, ‘Ba za ka haye Urdun ba.’
3
Ubangiji Allahnku kansa zai haye a gabanku. Zai hallaka waɗannan al’ummai da suke gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu. Yoshuwa shi ma zai haye a gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
4
Ubangiji zai yi da su, yadda ya yi da Sihon da Og, sarakunan Amoriyawa, waɗanda ya hallaka tare da ƙasarsu.
5
Ubangiji zai bashe su gare ku, dole kuma ku yi musu dukan abin da na umarce ku.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 90 chars

Options