Tsallake zuwa abun ciki
Maimaitawar Shari’a 24:19-22

Dokokin Tsintar Amfanin da ya Ragu da Sadaka

Maimaitawar Shari’a 24:19-22
19
Sa’ad da kuke girbi a gonarku, sai kuka manta da dami, kada ku koma don ku ɗauka. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa, saboda Ubangiji Allahnku yă albarkace ku a cikin dukan aikin hannuwanku.
20
Sa’ad da kuka kakkaɓe ’ya’yan zaitun daga itatuwanku, kada ku yi kalan abin da ya rage. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa.
21
Sa’ad da kuka yi girbin inabi a gonar inabinku, kada ku yi kalan abin da ya rage. Ku bar shi don baƙo, maraya da kuma gwauruwa.
22
Ku tuna dā ku bayi ne Masar. Shi ya sa na umarce ku ku yi wannan.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options