Kolossiyawa 3:1-3
1
Da yake an tashe ku tare da Kiristi, sai ku sa zukatanku a kan abubuwan da suke sama, inda Kiristi yake zaune a hannun dama na Allah.
2
Ku sa hankulanku a kan abubuwan sama, ba kan abubuwan duniya ba.
3
Gama kun mutu, ranku yanzu kuwa yana ɓoye tare da Kiristi a cikin Allah.