Ayyukan Manzanni 9:20-21
20
Nan take ya fara wa’azi cikin majami’u cewa Yesu Ɗan Allah ne.
21
Dukan waɗanda suka ji shi suka yi mamaki suka ce, “Ba shi ne mutumin da ya tā-da-na-zaune-tsaye a kan masu kira bisa ga wannan sunan a Urushalima ba? Ba ya zo nan ne don yă kai su a matsayin ’yan kurkuku ga manyan firistoci ba?”