Ayyukan Manzanni 4:21-22
21
Bayan ƙarin barazana sai suka bar su su tafi. Ba su iya yanke shawara yadda za a hore su ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
22
Gama mutumin da ya sami warkarwar banmamaki, shekarunsa sun fi arba’in.