Skip to content
Ayyukan Manzanni 14:14-18

Ayyukan Manzanni 14:14-18

14
Amma da manzannin nan Barnabas da Bulus suka ji haka, sai suka yayyage tufafinsu suka ruga cikin taron, suna ihu suna cewa,
15
“Ya ku mutane, don me kuke yin haka? Ai, mu ma mutane ne kawai, ’yan adam ne kamar ku. Mun kawo muku labari mai daɗi ne, muna gaya muku ku juya daga waɗannan abubuwa banza, ku juyo ga Allah mai rai, wanda ya yi sama da ƙasa da teku da kuma dukan abin da yake cikinsu.
16
A zamanin dā, ya bar dukan ƙasashe su yi yadda suka ga dama.
17
Duk da haka bai bar kansa babu shaida ba. Ya nuna alheri ta wurin ba ku ruwan sama da kuma amfanin gona a lokutansu; ya ba ku abinci mai yawa ya kuma cika zukatanku da farin ciki.”
18
Ko da waɗannan kalmomi ma, da ƙyar suka hana jama’an nan yin musu hadaya.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options