Skip to content
2 Sama’ila 5:17-21

2 Sama’ila 5:17-21

17
Da Filistiyawa suka ji labari an shafe Dawuda sarki a bisa Isra’ila, sai suka haura da ƙarfi sosai don su nema shi, amma Dawuda ya ji labarin sai ya gangara zuwa mafaka.
18
To, fa, Filistiyawa suka zo suka baje ko’ina a cikin Kwarin Refayim;
19
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In tafi in kai wa Filistiya hari? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Je ka, gama tabbatacce zan bashe Filistiyawa a hannunka.”
20
Saboda haka Dawuda ya tafi Ba’al-Ferazim, a can ya ci su da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa yakan fasu, haka Ubangiji ya kakkarya abokan gābana a gabana.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
21
Filistiyawa suka bar gumakansu a can, Dawuda da mutanensa kuwa suka kwashe su.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options