Skip to content
2 Korintiyawa 5:1-4

2 Korintiyawa 5:1-4

1
Yanzu mun san cewa in an hallaka tentin duniyan nan da muke ciki, muna da wani gini daga Allah, madawwamin gida a sama, wanda ba da hannuwan mutum ne suka gina shi ba.
2
Kafin nan muna nishi, da marmari a yi mana sutura da gidanmu na sama,
3
don sa’ad da aka yi mana sutura, ba za a same mu tsirara ba.
4
Sa’ad da muke zaune a cikin jikin nan na duniya, nishi muke domin matsuwar da muke sha, ba domin muna so mu rabu da jikinmu na wannan duniya ba ne, sai dai don so muke yi a suturta mu da na Sama, domin mai rai ya shafe mai mutuwa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options