2 Tarihi 25:27-28
27
Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
28
Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.