Skip to content
1 Sarakuna 17:2-7

Iliya a bakin rafin Kerit

1 Sarakuna 17:2-7
2
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce,
3
“Ka bar nan, ka nufi wajajen gabas, ka ɓuya a Rafin Kerit, gabas da Urdun.
4
Za ka sha daga rafin, zan kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can.”
5
Saboda haka sai Iliya ya yi abin da Ubangiji ya faɗa masa. Ya tafi Rafin Kerit, gabas da Urdun, ya zauna a can.
6
Hankaki suka riƙa kawo masa abinci da nama, safe da yamma, ya kuma sha daga rafin.
7
Ana nan sai rafin ya bushe saboda ba a yi ruwan sama a ƙasar ba.
Settings

Reading style

Typeface

Font size 19px

Reading width 90 chars

Options