Skip to content
1 Korintiyawa 3:18-23

1 Korintiyawa 3:18-23

18
Kada ku ruɗi kanku. In waninku yana tsammani cewa yana da hikima, yadda duniya ta ɗauki hikima, to, sai ya mai da kansa “wawa” don yă zama mai hikima.
19
Gama hikimar duniyan nan, wauta ce a gaban Allah, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yakan kama masu hikima a cikin makircinsu”;
20
kuma a rubuce yake cewa, “Ubangiji ya san dukan tunanin masu hikima banza ne.”
21
Saboda haka, kada wani yă yi taƙama da mutum! Gama kome naku ne,
22
ko Bulus ko Afollos ko Kefas ko duniya ko rai ko mutuwa ko abubuwa na yanzu ko na nan gaba, ai, duka naku ne,
23
ku kuwa na Kiristi ne, Kiristi kuma na Allah ne.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options