Skip to content
1 Korintiyawa 15:17-19

1 Korintiyawa 15:17-19

17
In kuwa ba a tashe Kiristi ba, bangaskiyarku a banza take, ya zama har yanzu kuna cikin zunubanku ke nan.
18
Ashe, waɗanda suka yi barci a cikin Kiristi ma sun hallaka ke nan.
19
In a wannan rayuwar ce kaɗai muke da bege cikin Kiristi, mun zama abin tausayi fiye da dukan mutane.

Duba kuma

Sauran wuraren da Nassi ya faɗi haka

  • Romawa 4:25

    An miƙa shi ga mutuwa saboda zunubanmu, aka kuma tashe shi zuwa rai saboda Allah zai same mu marasa laifi.
    daga aya ta 17
  • Ru’uya ta Yohanna 14:13

    Sai na ji murya daga sama ta ce, “Rubuta, Masu albarka ne matattun da suka mutu cikin Ubangiji daga yanzu zuwa gaba.” “I, za su huta daga faman aikinsu, gama ayyukansu za su bi su,” in ji Ruhu.
    daga aya ta 18
  • 1 Bitrus 1:3

    Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi! Cikin jinƙansa mai girma ya ba mu sabuwar haihuwa cikin bege mai rai ta wurin tashin Yesu Kiristi daga matattu,
    daga aya ta 17
  • 1 Bitrus 1:21

    Ta gare shi ne kuka gaskata da Allah, wanda ya tā da shi daga matattu, aka kuma ɗaukaka shi, ta haka bari bangaskiyarku da begenku su kasance ga Allah.
    daga aya ta 17
  • 1 Korintiyawa 15:14

    In ba a tashe Kiristi ba kuwa, ai, wa’azinmu, da bangaskiyarku banza ne.
    daga aya ta 17
  • 2 Timoti 1:12

    Shi ya sa nake shan wahalar da nake sha. Duk da haka ba na jin kunya, domin na san wanda na gaskata da shi, na kuma tabbata cewa yana iya kiyaye abin da na danƙa masa amana don wancan rana.
    daga aya ta 19
  • 1 Tessalonikawa 4:13

    ’Yan’uwa, ba ma so ku kasance cikin jahilci game da waɗanda suka yi barci, ko kuwa ku yi baƙin ciki kamar sauran mutanen da ba su da bege.
    daga aya ta 18
  • 1 Tessalonikawa 4:14

    Mun gaskata cewa Yesu ya mutu ya tashi kuma daga matattu, ta haka muka gaskata cewa Allah zai kawo waɗanda suka yi barci a cikinsa tare da Yesu.
    daga aya ta 18
  • 1 Korintiyawa 4:9

    Gama a ganina fa, Allah ya baje mu manzanni a ƙarshen jerin gwanon, a matsayin mutanen da aka hukunta ga mutuwa a filin wasanni. Mun zama abin kallo ga dukan duniya, ga mala’iku da kuma mutane.
    daga aya ta 19
  • 1 Korintiyawa 4:13

    in aka ɓata mana suna, mukan mayar da alheri. Har yă zuwa wannan lokaci, mu ne kamar jujin duniya, abin ƙyamar kowa.
    daga aya ta 19
  • Romawa 8:33

    Wa zai kawo wani zargi a kan waɗanda Allah ya zaɓa? Allah ne mai kuɓutarwa.
    daga aya ta 17
  • Romawa 8:34

    Wa zai yi hukunci? Yesu Kiristi ne, wanda ya mutu, fiye da haka ma, shi da aka tā da zuwa rai, yana zaune a hannun dama na Allah yana kuma yin roƙo a madadinmu.
    daga aya ta 17

Inda wannan ya faru

Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options