1 Tarihi 4:38-40
38
Mutanen da aka jera sunayensu a bisa, shugabannin gidajensu ne. Iyalansu sun ƙaru sosai,
39
suka tafi bayan garin Gedor wajajen gabashin kwari suna neman makiyaya domin garkunansu.
40
Suka sami makiyaya mai ciyawa mai kyau, ƙasar kuma tana da fāɗi, da salama, kuma zaman lafiya. A dā waɗansu mutanen Ham sun zauna a can.
Settings