Skip to content
Zakariya 6:1-4

Zakariya 6:1-4

1
Na sāke ɗaga kai sama, sai ga kekunan yaƙi guda huɗu a gabana suna fitowa tsakanin duwatsu guda biyu, duwatsun tagulla!
2
Karusa ta farko tana da jajjayen dawakai, ta biyu kuma baƙaƙen dawakai,
3
ta ukun farare dawakai, ta huɗu kuma dawakai masu ɗigo-ɗigo a dukan jikinsu, dukansu kuwa ƙarfafa.
4
Sai na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options